Fitaccen malamin addinin Musulunci na ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah wa Ikamatis-Sunnah (JIBWIS), Sheikh Muhammad Maibarga, ya rasu a hannun masu garkuwa da mutane bayan da aka sace shi a jihar Kebbi.
An sace marigayin tare da wani abokinsa, tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Koko/Besse, lamarin da ya jawo damuwa a tsakanin al’ummar yankin da mabiyansa.
An tabbatar da rasuwarsa a ranar Laraba, yayin da iyalansa da abokansa ke ci gaba da ƙoƙarin ganin an biya kuɗin fansa domin a kuɓutar da shi.
Rahotanni sun ce kafin rasuwarsa, masu garkuwar sun fitar da wani bidiyo da ke nuna malamin cikin mawuyacin hali na rashin lafiya, lamarin da ya ƙara tayar da hankalin jama’a yayin da ake ci gaba da tattaunawar kuɓutar da shi.
Kakakin rundunar yan sandan jihar Kebbi, SP Bashir Usman, ya tabbatar da cewa hukumomi sun samu rahotannin da ke nuna tabarbarewar lafiyar malamin da kuma rasuwarsa a hannun masu garkuwa.
Wani abokin marigayin, Usman Aliyu, ya ce iyalansa na ci gaba da ƙoƙarin tara kuɗin da masu garkuwar suka buƙata lokacin da aka samu labarin rasuwarsa.
A cewarsa, ana ci gaba da tattaunawa kan kuɓutar da malamin, kuma iyalansa na bakin ƙoƙarinsu wajen cika buƙatun masu garkuwar kafin wannan mummunan labari ya zo musu.
Rasuwar Sheikh Maibarga ta jefa iyalansa, abokansa, mabiyansa da al’ummar yankin cikin alhini, yayin da mutane da dama ke alhinin rasuwar malamin da ake girmamawa.
Lamarin ya sake fito da matsalar rashin tsaro a yankin Arewa maso Yammacin Najeriya, inda garkuwa da mutane domin neman kuɗin fansa da hare-haren yan bindiga ke ci gaba da zama babbar barazana ga rayuka da dukiyoyin al’umma.
