Shugaban Ƙasar Colombia, Gustavo Petro, ya shaida wa BBC cewa ya yi ammanar cewa Ƙasarsa na fuskantar barazanar harin soji daga Amurka.
Kalaman nasa na zuwa ne ‘yan kwanaki bayan da shugaba Trump ya ce kai wa Columbiya farmakin sojoji abu ne da zai haifar da kyakyawan sakamako.
A baya dai shugabannin biyu sun yi ta musayar kalaman ɓatanci tsakaninsu.
Sai dai sun yi magana a ranar Larabar data gabat inda suka shirya wani taro a Fadar White House.
A makon da ya gabata ne Amurkan ta kai wa Venezuela hari tare kuma da kama shugaban ƙasar Nicolas Maduro da mai ɗakinsa.
