An kubutar da ‘yan makaranta mata dalibai 25 da ‘yanbindiga suka sace a makarantar sakandare ta Mag a jhar Kebbi.
An sako daliban ne a ranar Talata da maraice.
Jaridar Cable ta wallafa hoton bidiyon daliban a motar safa kan hanyarsu na barin hannun wadanda suka yi garkuwa da su.
Wata majiya ta tabbatar da sakin ɗaliban ne bayan wani ƙoƙari na sasanci da Gwamnatin Tarayya ta yi ta hannun Ofishin Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro da Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS), waɗanda suka jagoranci tattaunawa da ɓangarorin da abin ya shafa.
- Za Mu Dauki Dukkan Matakai Don Ceto Daliban Kebbi – Gwamnatin Tarayya
- ‘Yan ta’adda sun sace dalibai 25 sun hallaka shugaban makaranta a Kebbi
Rahotanni sun ce gwamnati ta yi amfani da tsarin lumana ta hanyar sulhu ba tare da amfani da ƙarfin soja ba, wanda ya haɗa da tattaunawa wajen kuɓutar da ɗaliban.
‘Yan bindiga sun sace daliban 25 ne da asubahin ranar Litinin ta makon jiya ce a harin da suka kai Makarantar Sakandiren ’Yan Matan ta GGCSS Maga da ke Ƙaramar Hukumar Danko/Wasagu a Jihar Kebbi, inda suka yi awon da ɗaliban ke shirin tashi sallar asuba.
