Saurari premier Radio
33.9 C
Kano
Saturday, April 20, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiKiwon LafiyaZa a fara baiwa mata masu ciki alawus din 5,000 duk wata...

Za a fara baiwa mata masu ciki alawus din 5,000 duk wata a Jigawa

Date:

Mukhtar Yahya Usman

Gwamnatin Jihar Jigawa ta ce ta kammala shiri tsaf domin fara biyan mata masu juna biyu akalla su 5,000 da aka dauki bayanansu alawus din N5,000 a kowane wata.

Mataimakain Gwamanan Jihar, Mallam Umar Namadi, ne ya bayyana hakan yayin wata zantawarsa da manema labarai a Dutse, babban birnin Jihar.

Ya ce Jihar ta bullo da shirin ne domin ya taimaka wa mazauna yankunan karkara su rika zuwa awon ciki da kuma zuwa asibiti domin haihuwa.

Malam Umar ya kara da cewa tuni gwamnati ta sanya shirin a cikin kasafin kudinta na shekarun 2021 da 2022.

Mataimakain Gwamnan ya ce suna sa rana kudaden za su taimaka wa matan wajen sayen abincin da zai inganta lafiyarsu da ta ’ya’yan cikin nasu saboda kare su daga kamuwa da cutar yunwa.

Ya ce tuni aka bude wa kimanin mata 3,800 asusun ajiya na banki kuma za a fara biyansu a watan Fabrairun 2022, yayin da suke kokarin magance matsalar da ta shafi sauran ragowar mata 1,200.

Malam Umar Namadi ya ce an zabo matan ne daga mazabun siyasa 287 na Jihar domin fara shirin a matsayin gwaji, kafin daga bisani a fadada shi da zarar wannan ya samu nasara.

Latest stories

NPFL: Gwamnatin Kano ta bawa Kano Pillars wasa Uku domin ta yi Nasara

Gwamnatin Jihar Kano ta bawa kungiyar Kwallon kafa ta...

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Related stories

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Farashin Dizel ya koma 1000 a Najeriya

Rahotanni sun bayyana matatar mai ta Dangote ta sanar...