Saurari premier Radio
29.9 C
Kano
Saturday, April 20, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiYANZU-YANZU: Kotun koli ta tabbatar da Adeleke a matsayin gwamnan Osun

YANZU-YANZU: Kotun koli ta tabbatar da Adeleke a matsayin gwamnan Osun

Date:

Kotun koli ta tabbatar da Ademola Adeleke na jam’iyyar PDP a matsayin halastaccen wanda ya lashe zaben gwamnan jihar Osun.

Mai shari’a Emmanuel Agim, wanda ya karanta hukuncin a ranar Talata nan, ya tabbatar da hukuncin kotun daukaka kara, wadda ta tabbatar da nasarar zaben Ademola Adeleke.

Kwamitin alkalai mai mutune biyar na kotun koli, ya ce kotun daukaka kara da ta tabbatar da Adeleke a matsayin gwamna daidai ne.

Tunda fari dai, Oyetola da jam’iyyar sa ta APC sun garzaya kotun koli ne, inda suka roki kotun da ta yi watsi da hukuncin da kotun daukaka kara ta Abuja ta yanke wanda ya karyata hukuncin da kotun baya da ta yanke.

Idan za a iya tunawa kotun sauraren kararrakin zabe ta jihar Osun, wadda ta mayar da Oyetola a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan da aka yi a ranar 16 ga watan Nuwamba, 2022.

Latest stories

NPFL: Gwamnatin Kano ta bawa Kano Pillars wasa Uku domin ta yi Nasara

Gwamnatin Jihar Kano ta bawa kungiyar Kwallon kafa ta...

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Related stories

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Farashin Dizel ya koma 1000 a Najeriya

Rahotanni sun bayyana matatar mai ta Dangote ta sanar...