Mukhtar Yahya Usman
Ɗalibai a Kano sun fito zanga-zanga domin nuna rashin jin daɗinsu kan yajin aikin da ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta ASUU ke yike.
Sun fara tattakin ne daga karkashin gadar kofar Nasarawa, sannan suka shiga gidan Murtala don isar da sakonsu ga Kwamishiniyar da ke kula da manyan makarantu.
An samar da jami’an tsaro na DSS da ƴan Sanda daga ƙofar Nasarawa zuwa dukkan mahaɗa ta zuwa gidan gwamnatin Kano, da karkashin gadar Nasarawa.
Tun a makon jiya ƙungiyar ɗaliban ta ƙasa NANS ta ce za ta ƙaddamar da zanga-zanga a manyan biranen kasar nan kan yajin aikin ASUU.