Saurari premier Radio
34.3 C
Kano
Monday, September 25, 2023
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiWasanniOsimhen ka iya zama dan Afrika na gaba da zai lashe Ballon...

Osimhen ka iya zama dan Afrika na gaba da zai lashe Ballon d’Or — Weah | Premier Radio | 10.05.2023

Date:

Shugaban kasar Liberia George Weah ya taya murna ga Dan wasa Victor Osimhen, wanda ya taimakawa Napoli lash gasar Serie A a karon farko tin shekaru 33 da suka gabata.

Osimhen ya Kuma zama dan wasan nahiyar Afrika mafi yawan zura kwallo a wata gasa a kasar Italiya.

Wannan na zuwa ne bayan da Osimhen ya zura kwallo, a wasan da Napoli tayi nasara kan Fiorentina da ci 1-0 a karshen mako.

Kuma ya kamo tarihin yawan zura kwallo da jumulla 47 a gasar Serie A, ma’ana ya zarta Weah wanda ya zura kwallo 46 lokacin da yake AC Milan.

Dan wasan Napoli a ranar Litinin, a shafinsa na Twitter ya wallafa jindadinsa na kasancewa dan wasan mafi yawan zura kwallo, wanda ya samu damar kamo tarihin Weah.

Sai dai kuma a martanin da ya yi mishi Mai shekara 56 Weah ya taya Dan wasan murnan samun wannan nasara, yana Mai cewa da sannu Osimhen ka iya zama Dan wasa na gaba da zai lashe kyautar Ballon d’Or a nan gaba.

Latest stories

Related stories

Abu uku da ya kamata ku sani a gasar Champions League ta 2023/2024

Tuni a wannan rana ta Talata 19 ga Satumbar...

NFCA reshen Kano ta taya Abdu Maikaba murnan zama sabon kocin Kano Pillars

Kungiyar Masu horarwa ta kasa reshan jahar Kano (...