Hukumar kula da jiragen kasa ta kasa(NRC) ta dakatar da jigilar fasinjoji daga Abuja zuwa Kaduna sakamakon gocewa daga layin dogo da wani jirgi ya yi a ranar Juma’a.
Daraktan NRC Niyi Alli ne ya bayyana hakan ga manema labarai.
Mista Alli yace “Da Taimakon Ubangiji ba a samu wanda ya yi rauni ba ko daya, sai dai duk da haka muna neman afuwar al’ummar da wannan tsaiko na jigilar jirgin zai shafa”
Ya kuma tabbatar da cewa tuni hukumar NRC ta fara kokarin shawo kan matsalar.
Wannan dai na zuwa ne kwanaki kadan bayan dawo da zirga-zirgar jirgin tun bayan dakatar da shi sakamakon sace fasinjojin da ’yan bindiga suka yi a watan Maris na bara.