Mukhtar Yahya Usman
Al’ummar China mazauna Kano sun bukaci a hukunta dan kasarsu da ake zargi da kisan wata mata ‘yar Kano mai suna Ummukulsun Buhari a unguwar Jambulo.
Wannan na kunshe cikin wata samarsa da Wakilin Mutanen China a Kano Mike Zhang ya fitar ranar Litinin a Kano.
Sanarwar ta yi Allah wadai da kisan matashiyar, kuma ta bukaci a hukunta shi dai-dai da abinda ya aikata.
Haka zalika ta bukaci mahukunta su gudanar da binciken kwakwafi kan lamari daga dukkanin bangarorin jami’an tsaro.
Sanarwar ta ce al’ummar China a Kano na bin dukkanin dokokin kasa kuma suna bin duk dokar da aka gindaya musu.
Su kuma nuna jin dadinsu kan irin damar da aka basu suke zaune a Kano ba tare da takuraba.
Al’ummar ta kuma mika sakon ta’aziyyarta ga iyalai da dangin mamaciyar inda suka roki Allah ya gafarta mata.