Saurari premier Radio
33.9 C
Kano
Thursday, April 25, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiMuna so a hukunta dan uwanmu da ya kashe Ummita-‘Yan China mazauna...

Muna so a hukunta dan uwanmu da ya kashe Ummita-‘Yan China mazauna Kano

Date:

Mukhtar Yahya Usman

 

Al’ummar China mazauna Kano sun bukaci a hukunta dan kasarsu da ake zargi da kisan wata mata ‘yar Kano mai suna Ummukulsun Buhari  a unguwar Jambulo.

 

Wannan na kunshe cikin wata samarsa da Wakilin Mutanen China a Kano Mike Zhang ya fitar ranar Litinin a Kano.

 

Sanarwar ta yi Allah wadai da kisan matashiyar, kuma ta bukaci a hukunta shi dai-dai da abinda ya aikata.

 

Haka zalika ta bukaci mahukunta su gudanar da binciken kwakwafi kan lamari daga dukkanin bangarorin jami’an tsaro.

 

Sanarwar ta ce al’ummar China a Kano na bin dukkanin dokokin kasa kuma suna bin duk dokar da aka gindaya musu.

 

Su kuma nuna jin dadinsu kan irin damar da aka basu suke zaune a Kano ba tare da takuraba.

 

Al’ummar ta kuma mika sakon ta’aziyyarta ga iyalai da dangin mamaciyar inda suka roki Allah ya gafarta mata.

 

Latest stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...

Related stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...