Saurari premier Radio
38.9 C
Kano
Thursday, April 25, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiJirgin Farko Na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya.

Jirgin Farko Na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya.

Date:

Jirgin farko na maniyyatan jihar Jigawa ya yi saukar gaggawa a filin jirgin saman Malam Aminu Kano.

Jirgin na kamfanin Max Air kirar Boeing 747 da ya taso daga filin jirgin saman Dutse da ke jihar Jigawa, ya dakatar da tafiya zuwa kasar Saudiyya a lokacin da ya samu da matsalar.

Wata maniyyaciyya da ta ce suna zaune a cikin jirgi ana kokarin sauya musu wani jirgin don ci gaba da tafiya.

A cewarta, matsalar ta afku ne sakamakon kankarar ruwan sama da ta bugi gilashin jirgin lamarin da ya janyo tsagewarsa.

Hakan dai ya tilastawa jirgin fasa tafiya kasar ta Saudiyya tare da juyowa nan Kano.

Kawo yanzu dai babu wani jami’i da ya magantu kan hakan.

Latest stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...

Related stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...