Saurari premier Radio
33.9 C
Kano
Friday, April 19, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiJami’ar Bayero Ta Musanta Kara Kudin Makaranta Ga Dalibai.

Jami’ar Bayero Ta Musanta Kara Kudin Makaranta Ga Dalibai.

Date:

Hukumar gudanarwar Jami’ar Bayero Kano ta musanta labarin cewa ta kara kudin makaranta ga dalibanta da kuma wadanda ke son shiga.

 

Cikin wani sautin murya da mai magana da yawun Jami’ar, Malam Lamara Garba, ya aikowa Premier radio, yace labarin ba gaskiya bane, don haka ya bukaci iyayen dalibai, da sauran masu ruwa da tsaki da su kwantar da hankulansu.

 

Ya kara da cewa har yanzu jami’ar bata samar da matsaya ba, kan kudin da ya kamata dalibai su biya a bana.

 

Tuni dai wasu jami’o’i musamman na gwamnatin tarayya ke ci gaba da kara kudin makaranta ga dalibai, wanda hakan ya haifar da damuwa ga daliban da iyayensu.

Latest stories

NPFL: Gwamnatin Kano ta bawa Kano Pillars wasa Uku domin ta yi Nasara

Gwamnatin Jihar Kano ta bawa kungiyar Kwallon kafa ta...

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Related stories

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Farashin Dizel ya koma 1000 a Najeriya

Rahotanni sun bayyana matatar mai ta Dangote ta sanar...