Saurari premier Radio
32.9 C
Kano
Thursday, April 25, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiJami’ar Bayero Ta Musanta Kara Kudin Makaranta Ga Dalibai.

Jami’ar Bayero Ta Musanta Kara Kudin Makaranta Ga Dalibai.

Date:

Hukumar gudanarwar Jami’ar Bayero Kano ta musanta labarin cewa ta kara kudin makaranta ga dalibanta da kuma wadanda ke son shiga.

 

Cikin wani sautin murya da mai magana da yawun Jami’ar, Malam Lamara Garba, ya aikowa Premier radio, yace labarin ba gaskiya bane, don haka ya bukaci iyayen dalibai, da sauran masu ruwa da tsaki da su kwantar da hankulansu.

 

Ya kara da cewa har yanzu jami’ar bata samar da matsaya ba, kan kudin da ya kamata dalibai su biya a bana.

 

Tuni dai wasu jami’o’i musamman na gwamnatin tarayya ke ci gaba da kara kudin makaranta ga dalibai, wanda hakan ya haifar da damuwa ga daliban da iyayensu.

Latest stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...

Related stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...