Saurari premier Radio
38.9 C
Kano
Thursday, April 25, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiGobarar Kasuwa: Gwamna Zulum ya gamu da fushin matasa | Premier Radio...

Gobarar Kasuwa: Gwamna Zulum ya gamu da fushin matasa | Premier Radio | 26.02.2023

Date:

Daruruwan shaguna rahotanni ke bayyana cewa sun kone kurmus, hadi da kayayyaki masu darajar miliyoyin naira, biyo bayan tashin gobara a babbar kasuwar Borno, wadda aka fi sani da kasuwar Litinin.

Wasu majiyoyi sun ce gobarar ta tashi ne da misalin karfe 2 na daren jiya.

Zuwa yanzu, babu asarar rai da aka samu, yayinda yan kwana-kwana ke cigaba da aikin kashe wutar.

Har ila yau babu cikakken bayani game da musabbabin tashin ta, to amma, ba wannan ne karon farko da ake samun billar gobara a kasuwar ba.

Tuni dai gwamnan Borno, Farfesa Babagana Zulum ya ziyarci kasuwar, inda fusatattun matasa suka rika jifansa da duwatsu, sannan suna yi masa ihun ‘bama yi’.

Lamarin sai da ya kai jami’an tsaro ga harbe harben iska, da kuma jefa hayaki mai sa hawaye don tarwatsa matasan.

Latest stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...

Related stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...