Saurari premier Radio
32.9 C
Kano
Thursday, April 25, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiGwamnatin KanoDuk da janye gayyata, Buhari ya toge kan zuwa Kano | Premier...

Duk da janye gayyata, Buhari ya toge kan zuwa Kano | Premier Radio | 29.01.2023

Date:

Muhammad Bello Dabai

 

Duk da janye gayyatar da gwamnatin Kano ta yi wa shugaban kasa Muhammadu Buhari domin bude wasu ayyuka da ta yi, da alama shugaban na nan tafe a ranar Litinin.

 

A wani sako mai harshen damo da mataimakin shugaban kan kafafen sada zumunta, Bashir Ahmad ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya tabbatar da cewa Buhari na tafe a gobe Litinin.

 

Har ila yau, a wani sakon na daban, Bashir Ahmad yace duk wani mai shirin jifan shugaba Buhari a jihar Kano, to babu hannun Kanawa a ciki.

Da fari dai, gwamnatin Kano ta janye gayyatar da ta yi wa shugaban ne, biyo bayan jifan da tawagarsa ta sha a jihar Katsina.

 

Hakan dai ba zai rasa nasaba da batun sauyin takardun naira 200, 500 da kuma 1000 da gwamnatinsa ta toge akan sai ya tabbata ba.

 

Yanzu haka kwanaki 2 suka rage wa’adin dena karbar tsaffin takardun ya cika, wanda hakan ke nufin ga duk wanda bai sauya kudinsa ba, to zai tafka asara.

 

Lamarin a yanzu, ya haddasa tsayawar kasuwanci cak a wasu kasuwannin, sabida dakatar da tsaffin takardun da tuni wasu yan kasuwa suka yi, gabanin cikar wa’adin da babban bankin kasar CBN ya bayar.

 

 

Latest stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...

Related stories

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...