Saurari premier Radio
38.9 C
Kano
Friday, April 19, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiBuhari ya karawa malaman makaranta wa'adin ritaya

Buhari ya karawa malaman makaranta wa’adin ritaya

Date:

Shugaban kasa Buhari ya sanya hannu kan dokar karawa malaman makaranta shekarun ajiye aiki zuwa 65.

Mai taimakawa shugaban kan kafafen yada labarai Malam Garba Shehu, ne ya bayyana haka a ranar Juma’a a Abuja.

Gwamnatin tarayya ta amince da dokar karawa malaman wa’adin yin ritaya ne a watan Janairun bara inda kuma shugaban kasa ya aikewa majalissun dokoki na tarayya dokar a watan Yunin na bara inda bayan da suka amince da dokar ne kuma ya sanya mata hannu.

Sashin farko na dokar yace malamai a kasar nan sai sun shekara 65 zasu ajiye aiki maimakon shekaru sittin da ma’aikatan gwamnati ke ajiye aiki.

2023: Malamai su daina yiwa ‘yan siyasa addu’a don neman kudi-Muhammadu Sanusu II
Haka zalika dokar ta ce malamin makaranta zayyi ritaya ne yayin da ya shekara 40 yana aiki maimakon shekara 35 kamar sauran ma’aiakatan gwamnati.

Latest stories

NPFL: Gwamnatin Kano ta bawa Kano Pillars wasa Uku domin ta yi Nasara

Gwamnatin Jihar Kano ta bawa kungiyar Kwallon kafa ta...

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Related stories

Dan Ganduje ya kai wa Muhuyi ziyarar goyan bayan a binciki mahaifansa

Dan tsohon gwamnan Kano, Abdulaziz Abdullahi Ganduje, ya kai...

Farashin Dizel ya koma 1000 a Najeriya

Rahotanni sun bayyana matatar mai ta Dangote ta sanar...