Shugaban kasa Buhari ya sanya hannu kan dokar karawa malaman makaranta shekarun ajiye aiki zuwa 65.
Mai taimakawa shugaban kan kafafen yada labarai Malam Garba Shehu, ne ya bayyana haka a ranar Juma’a a Abuja.
Gwamnatin tarayya ta amince da dokar karawa malaman wa’adin yin ritaya ne a watan Janairun bara inda kuma shugaban kasa ya aikewa majalissun dokoki na tarayya dokar a watan Yunin na bara inda bayan da suka amince da dokar ne kuma ya sanya mata hannu.
Sashin farko na dokar yace malamai a kasar nan sai sun shekara 65 zasu ajiye aiki maimakon shekaru sittin da ma’aikatan gwamnati ke ajiye aiki.
2023: Malamai su daina yiwa ‘yan siyasa addu’a don neman kudi-Muhammadu Sanusu II
Haka zalika dokar ta ce malamin makaranta zayyi ritaya ne yayin da ya shekara 40 yana aiki maimakon shekara 35 kamar sauran ma’aiakatan gwamnati.