Saurari premier Radio
43.9 C
Kano
Wednesday, April 24, 2024
Saurari Premier Radio
HomeLabaraiAn gano jaririyar da aka sace daga Neja a Kano

An gano jaririyar da aka sace daga Neja a Kano

Date:

An gano wata jaririyar mai kimanin wata hudu a duniya, da aka sace daga kauyen Daga na Karamar Hukumar Tafa a Jihar Neja, a Jihar Kano.

Premier Radio ta ruwaito mahaifiyar jaririyar, Fatima Kabir, ta ce an sace jaririyarne mai suna Samhat a ranar Juma’ar da ta gabata.

Fatima dai ta garzaya Kano ne ranar Alhamis, lokacin da aka nuna mata wani hoto da ke cigiyar ’yartata a dandalin sada zumunta na Facebook a Jihar Kano.

Wani abokin mijin Fatiman, Ado Musa, a zantawarsa da Daily trust ya ce sai dai murnarsu ta koma ciki ne bayan da Dagacin da aka tsinci yarinyar a yankinsa ya ki yarda ya basu ita.

Ya ce har Hakimin Dakwa, Alhaji Alhassan Musa da kansa ya kira daya daga cikin mutanen da ke kula da lamarin a Kano, amma ya ce sun dauki matakin ne bayan wani shi ma ya yi ikirarin cewa jaririyar ’yarsa ce.

Hakimin na Dakwa dai ya ce tuni ’yan sanda suka shiga lamarin, inda dukkan bangarorin suka amince a yi gwajin kwayar halitta na DNA, don gano hakikanin iyayenta.

Latest stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...

Related stories

Hukumar EFCC ta musalta zargin da ake mata na fara bincikar tsohon Gwamnan kogi.

Shugaban hukumar EFCC mai hukunta masu yiwa tattalin arziki...

Majalisar dokokin Kano ta nemi a dakatar da KEDCO kan yanke wuta.

Majalisar Dokokin jihar Kano ta bukaci gwamnatin jihar data...